Akpabio ya dawo gida bayan jita jitar rashin lafiya ta kwantar da shi a Landan
Shugaban majalisar dattawan Najeriya, Sanata Godswill Akpabio, ya dawo ƙasar bayan hutun da ya yi a birnin Landan.
Rahotanni sun nuna cewa Akpabio ya sauka da sassafe a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe na birnin Abuja a safiyar Litinin.