Mukaddashin Gwamnan Jihar Katsina, Farouk Lawal Jobe, ya roƙi Shugaba Bola Tinubu ya gaggauta ɗaukar matakai na musamman wajen kawo ƙarshen hare-haren ’yan bindiga da suka ƙara ta’azzara a jihar.
Wannan roƙo na zuwa ne bayan wani mummunar harin da aka kai wa al’ummar Mantau, karamar hukumar Malumfashi, inda ’yan bindiga suka kashe mutane 13 a masallaci yayin da suke salla da safiyar Talata.