Akalla mutane shida sun rasu, yayin da wasu uku suka ɓace a hatsarin kwale-kwale da ya auku a Garin Faji, karamar hukumar Sabon Birni, jihar Sokoto.
Lamarin ya faru ne da safiyar Alhamis, 21 ga watan Agusta, lokacin da mazauna yankin ke tserewa daga farmakin da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai.