Yan bindiga sun kashe mutane biyu kauyen Dudaye, karamar hukumar Augie a jahar Kebbi.
Monday, 01 Sep 2025 00:00 am

Nagari Radio

Maudu’i Korafi Kan Matsalar Tsaro a Karamar Hukumar Augiu 

‎Mai Girma Gwamna, 

‎Ina rubuto wannan takarda ne don nuna matukar damuwa da bakin ciki game da halin rashin tsaro da ake fuskanta a Karamar Hukumar Augie. Lamarin ya kai wani mataki mai tayar da hankali, musamman da yawaitar hare-haren 'yan bindiga da sace-sacen mutane. 

‎Wani Al’amari na Musamman:

‎A ranar 30 ga Agusta, 2025, a kauyen Dudaye, mutane biyu sun rasa rayukansu sakamakon harin 'yan bindiga. 

‎Tasirin Lamarin

‎Mutane da dama sun bar gidajensu 

‎Harkokin kasuwanci sun tsaya cik 

‎Tsoro da firgici sun mamaye zukatan jama'a