
Yadda mutane ke rayuwa cikin fargaba a garuruwan da Boko Haram ke iko da su
A jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya, bayanai na nuna cewa akwai wasu yankunan na wasu ƙananan hukumomin jihar da ƙungiyar Boko Haram ko Iswap ke nuna ƙarfin iko.
Â
A ƙarshen makon da ya gabata ne Sanata Ali Ndume, ɗan majalisar dattijai daga jihar Borno ya bayyana wa manema labarai a Abuja cewa ƙananan hukumomin jihar uku na cikin irin wannan hali a yanzu haka.
Â
Ƙananan hukumomin sun haɗa da Gudumbari da Marte da kuma Abadam.
Â
A baya-bayan nan gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya yi ƙorafin cewa hare-haren Boko Haram da Iswap na ƙaruwa a jihar.
Â
Yana mai kira ga gwamnatin tarayya ta ɗauki mataki kafin lamarin ya yi ƙamari.
Â
Wasu daga cikin al'umomin waɗannan garuruwa sun shida wa BBC cewa sun shafe tsawon fiye da shekara shida suna rayuwa a ƙarƙashin ikon Boko Haram, kuma kowace rana suna cikin fargaba.
Â
Wani mazaunin Gudumbari, da ya buƙaci a sakaya sunansa saboda dalilai na tsaro, ya shaida wa BBC cewa tun 2018, ba su ƙara samun taimakon sojojin Najeriya ba.
Â
Ya ce suna rayuwa ne ƙarƙashin ikon mayaƙan - waɗanda suka kai hari tare da lalata wani sansanin sojin yankin da ya kamata ya kare ƙauyukan ƙaramar hukumar Gudumbari.
Â
"Tun 2018 lokacin da suka lalata sansanin soji, kusan ƙauyuka 10 ne suka faɗa hannun Boko Haram da ƙungiyar Iswap.
Â
"A yanzu haka, shalkwatar ƙaramar hukumar Gudumbari ce kawai ke hannun sojoji, amma kusan duka ƙauyukan ƙaramar hukumar na ƙarƙashin ikon ƴanta'addan,'' in ji shi.
Â
Ya ce, ''Kullum mutane na cikin fargaba, saboda kodayaushe suna ganin ƴan ta'addan na sintiri da harkokinsu a waɗannan ƙauyuka.''
Â
Ya ƙara da cewa Boko Haram da ƙungiyar Iswap na karɓar haraji da kayan abinci daga hannun manoma, saboda galibi al'ummar yankunan manoma ne.
Â
"Lokaci zuwa lokaci suna zuwa karɓar haraji, musamman bayan girbe amfanin gona, haka ma suna zuwa karɓar haraji daga hannun mutane.''
Â
Ya shaida wa BBC cewa a wasu lokuta sukan hukunta mutanen da suka aikata ba daidai ba.
Â
"Idan mutum ya aikata wani laifi, sukan hukunta shi, ciki har da zanewa."
Â
Ya ci gaba da cewa a halin da ake ciki yanzu haka babu wanda ya isa ya fita daga ƙaramar hukumar zuwa birnin Maiduguri, saboda matsalar tsaro.
Â
"Idan ka ga mutum ya fito daga Maiduguri zuwa Gudumbari, to sai dai idan yana cikin tawagar gwamna ko cikin rakiyar sojoji,'' a cewar mutumin.
Â
'Babu kowa a garin Abadam sai sojoji'
A yankin ƙaramar hukumar Abadam kuwa, lamarin ya fi muni saboda kusan duka fararen hula a garin sun tsere, saboda matsalar tsaron.
Â
Wata majiya ta shaida wa BBC cewa a yanzu haka in banda sojoji babu wani mutum da ke rayuwa a shalkwatar ƙaramar hukumar.
Â
"A yanzu sojoji ne kawai suka rage a shalkwatar ƙaramar huumar saboda kusan kowa ya fice daga garin don tsira da rayuwarsa.''
Â
"Kusan rabin mutanen ƙaramar hukumar sun tsare zuwa Jamhuriyar Nijar inda suka zama ƴan gudun hijria, yayin da sauran mutanen suka warwatsu zuwa makwabtan jihohi.''
Â
Majiyar ta kuma ce a yanzu mutanen ba su iya bin hanyar zuwa birnin Maiduguri, maimakon haka sun gwammace bin hanyar shiga Jamhuriyar Nijar.
Â
'Ko kayan abinci ba ma iya saya sai da rakiyar sojoji'
Can ma a ƙaramar hukumar Marte, mutanen yankin na ci gaba da tsarewa.
Â
Wani mazaunin garin, mai suna Babagana Ali, ya ce a yanzu haka babu kowa a tsohon garin Marte.
Â
"A yanzu haka babu wani mutum da ya rage a tsohon garin Marte. Galibi sun koma garin Sabon Marte mai nisan kilomita 12 daga tsohon garin.''
Â
Ya ci gaba da cewa mutanen da ke zaune a yankin na rayuwa cikin fargabar, saboda a cewar mayaƙan Boko Haram na kai musu hari.
Â
"Mutane na rayuwa cikin fargaba saboda lokaci zuwa lokaci mayaƙan na kai musu hari a garin na Sabon Marte da suke ciki a yanzu.''
Â
Ya ƙara da cewa wata matsalar da mutanen garin ke fuskanta ita ce ba sa iya fita zuwa garin Dikwa mai makwabtaka domin sayen kayan abinci.
Â
"Mutane ba sa iya fita domin sayo kayan abinci, har sai ƙarshen wata lokacin da sojoji za su yi musu rakiya cikin ayari.''
Â
Mazauna garuruwan sun yi kira ga gwamnati da sauran mutanen da za su iya taimakawa don kawo musu zaman lafiya a yankunansu.
Â
Jihar Borno ta shafe fiye da shekara 15 tana fama da matsalar tsaro mai alaƙa da Boko Haram, inda take kai hare-hare kan jami'am tsaro da fararen hula, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar ɗaruruwan mutane tare da raba dubbai da muhallansu.
Abdulrahman Abubakar