
Me ya jawo ƙaruwar matsalar tsaro a Najeriya?
Mazauna yankuna da wasu gwamnatocin jiha a sassan Najeriya na bayyana yadda matsalolin tsaro ke ƙara ta'azzara a kwanan nan, ciki har da ƙaruwar hare-haren masu iƙirarin jihadi.
Â
Lamarin ya ɗan fi ƙamari a arewaci zuwa tsakiyar Najeriya.
Â
Tun mako biyu da suka wuce mazauna wasu yankuna na jihar Filato da ke tsakiyar ƙasar suka auka cikin bala'i sakamakon hare-haren 'yanbindiga da ake alaƙantawa da ƙabilanci.
Â
Daga ƙarshen makon da ya gabata zuwa wannan kuma mazauna yankunan jihar Binuwai mai maƙwabtaka suka fuskanci sababbin hare-hare, waɗanda suka yi sanadiyyar kashe sama da mutum 70.
Â
Wani rahoto da kamfanin Beacon mai nazarin al'amuran tsaro a Najeriya da yankin Sahel ya fitar a watan Afrilu ya nuna cewa an samu ƙaruwar mutanen da aka kashe a cikin wata uku na farkon 2025 idan aka kwatanta da wata ukun ƙarshe na 2024.
Â
Rahoton ya ce an kashe mutum 3,610 a tsakanin watan Janairu zuwa Maris, lamarin da ya zarta yawan mutanen da aka kashe daga watan Oktoba zuwa Nuwamban 2024.
Â
A ranar Talata mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, ya kai ziyara jihar Binuwai, inda ya faɗa wa mutanen jihar cewa "za mu kawo ƙarshen matsalar nan, kada ku ji cewa ku kaɗai ne - lamarin ya shafe mu baki ɗaya".
Â
Â
da aka kai a jihar
Kaduna: An kashe mutum 106, a hare-hare 128 da aka kai a jihar
'Kada a siyasantar da kashe-kashe'
Akasarin kashe-kashen na baya-bayan nan sun faru ne a lokacin da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ke balaguro a ƙasashen Faransa da Birtaniya, abin da ya jawo 'yan'adawa suka yi ta sukarsa.
Â
Wani abu 'yan'adawar suka dinga sukar shugaban shi ne yadda ya ƙi miƙa ragamar mulkin ƙasar ga Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima, sai dai fadar shugaban ta ce ya ci gaba da aikinsa na shugaban ƙasa daga can.
Â
Yayin ziyarar da ya kai jihar Binuwai a ranar Talata, mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro Nuhu Ribadu ya ce Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ne ya umarce shi da ya yi hakan.
Â
Ya nemi duka ɓangarori a jihar da su kada su mayar da kashe-kashen siyasa.
Â
"Ku ba mu dama wajen daina siyasantar da kashe-kashen nan. Ba zai yiwu a tura jami'an tsaro kowane lungu ba, amma suna yin bakin ƙoƙarinsu," a cewarsa yayin wani taron manema labarai.
Â
"Wannan ba maganar siyasa ba ce, ko addini, ko ƙabila - zallan rashin imani ne. Ƙasashe da yawa a duniya kamar Sudan, Nijar, Mali, Burkina Faso na fama da irin wannan matsalar ko fiye da haka."