Ko sauya sheƙa zai iya durƙusar da jam'iyyar PDP?

Abubuwa na ta sauyawa a siyasar Najeriya, musamman a baya-bayan nan da aka samu yawaitar ƴan siyasa da ke ficewa daga babbar jam'iyyar adawa ta ƙasar - PDP.

 

Ficewar gwamnan jihar Delta, Sheriff Oborevwori daga PDP zuwa APC ta sanya a yanzu yawan gwamnonin jam'iyyar sun ragu.

 

A Litinin ɗinnan ne mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima da shugaban jam'iyyar APC Abdullahi Umar Ganduje da kuma sauran ginshiƙan jam'iyyar suka karɓi gwamnan.

 

Wannan ya sanya a yanzu APC ke da gwamnoni uku daga cikin shida a shiyyar Kudu maso kudancin Najeriya, yankin da a baya jam'iyyar PDP ke da ƙarfi cikinsa tsawon shekara 20.

 

A yanzu jihohin Cross River da Edo da Delta duk sun koma hannun APC, yayin da Rivers da Akwa Ibom da Bayelsa ke hannun jam'iyyar hamayyar ta PDP.

 

Sai dai wasu rahotannin na cewa akwai yiwuwar wasu gwamnonin na PDP za su sauya sheƙa.

 

PDP ita ce babbar jam'iyyar adawa a Najeriya, sai dai rikice-rikicen cikin gida ya yi mata dabaibayi, lamarin da ake ganin ya hana ta taka rawar da ta kamata a ɓangaren adawa.

 

Haka nan kasancewar É—aya daga cikin manyan Æ´aÆ´anta - Nyesom Wike - a cikin gwamnatin APC ta Bola Tinubu ya sanya wasu ke zargin ta da kasancewa tamkar "wani reshe na jam'iyyar APC".

 

Duk da cewa wasu manyan ƴan siyasa a Najeriyar sun nuna alamun cewa za su haɗe domin samar da adawa mai ƙarfi a zaɓen 2027, gwamnonin PDP a taron da suka yi na baya-bayan nan sun nesanta kansu daga haka.

 

Sai dai ficewar da Æ´aÆ´an jam'iyyar ke yi da kuma karkatar da wasu daga cikin jigajiganta, kamar Atiku Abubakar ke yi ga batun haÉ—akar Æ´an hamayya ba abin da jam'iyyar za ta so ne ba.

 

Shin wace irin illa hakan zai yi wa PDP?

"Tabbas, PDP na neman ta rasa ƙarfinta a Najeriya duba da yanayin yadda jihohin da jam'iyyar ta mallaka a 2015 da kuma yadda suke yanzu," in ji Lekan Ige, masani a fannin siyasa, a wata hira da BBC.

 

"A shekarar 2015, PDP ta mallaki jihohi 11, amma yanzu, bayan canjin gwamnan jihar Delta, sun rage zuwa 10. Kuma jita-jita na cigaba da yaÉ—uwa cewa gwamnonin Akwa Ibom da Rivers na iya canza jam'iyya su shiga APC nan ba da jimawa ba.

 

"Akwai wani lokaci a wannan ƙasa da PDP ta shugabanci ɓangaren zartarwa da kuma majalisar tarayya, amma yanzu ta zama jam'iyyar adawa. Saboda haka ta bayyana ƙarara cewa PDP ta rasa ƙarfin ikonta a Najeriya." In ji Ige.

 

Har wa yau, masanin ya ƙara da bayanin cewa " babbar illar sauya sheƙar ƴan PDP zuwa jam'iyya mulki shi ne yadda abin ke faruwa a daidai lokacin da ya kamata su haɗe kansu su tunkari APC. Amma yanzu a yadda ake tafiya da wuya jam'iyyar ta iya taɓuka wani abin arziƙi a kakar zaɓe mai zuwa ta 2027. Abin da ke nuna ƙarara cewa jam'iyyar ta durƙushe."


Comment As:

Comment (0)