
Shettima, Atiku, Sarkin Musulmi, Dangote, Manyan Najeriya sun hadu a taron zuba jari a Taraba
Jihar Taraba - Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, ya isa birnin Jalingo domin wakiltar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a taron zuba jari da ake gudanarwa a Taraba a bana. Taron na da nufin jawo hankalin masu zuba jari da masu ruwa da tsaki kan tattalin arziki domin yin hadin gwiwa da jihar.Â
Â
Tun a kwanakin baya gwamnatin jihar Taraba ta bude shafin yanar gizo domin yin bayani kan lamuran da suka shafi taron.Â
Â
Taron ya tara manyan ’yan kasuwa, ’yan siyasa da shugabanni daga sassa daban-daban na kasar, ciki har da tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Atiku Abubakar da Sarkin Musulmi. Manyan Najeriya sun je taron tattali a Taraba Taron ya zama wata dama ta musamman wajen nunawa duniya irin albarkatun da jihar Taraba ke da su musamman a fannin noma, makamashi da hakar ma’adanai An bayyana cewa hakan na da tasiri wajen bunkasa tattalin arzikin Arewa maso Gabas da ma kasa baki daya.Â
Â
Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar da manyan ’yan kasuwa irinsu Alhaji Aliko Dangote da Tony Elumelu sun halarci taron.Â
Â
Me ake fata a taron tattali na Taraba? An bayyana cewa babban muradin taron shi ne kirkiro hadin gwiwa tsakanin masu zuba jari da jihar domin samar da cigaba da zai dade yana amfani.Â
Â
Gwamnatin jihar ta bayyana cewa Taraba na da arzik
i da dama da har yanzu ba a taba amfani da su yadda ya kamata ba, musamman a fannonin noma da makamashi da ma’adanai.Â
Â
A lokacin taron aka samu halartar wasu gwamnoni irinsu Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago da mataimakin gwamnan Bauchi, da wasu ministoci daga gwamnatin tarayya.