
An kama matukin babur dauke da ĆuĆunan kan mutane a ogun
Rundunar âyan sanda a Jihar Ogun ta ce, ta kama wani mai babur mai suna Kadir Owolabi, yana Éauke da ĆoĆunan kan mutane uku.
Mai magana da yawun rundunar, CSP Omolola Odutola ce ta bayyana hakan a wata sanarwa da ta fitar a Abeokuta ranar Talata.
Odutola ta ce, binciken da jamiâan âyan sandan tafi da gidanka suka yi a jakar wanda ake zargin, ya kai ga gano wasu kan mutane guda uku.
Ta ce, jamiâan tsaro ne suka gudanar da aikin bincike na yau da kullum daga rundunar âyan sanda na tafi da gidanka na 71 PMF, a yankin Awa da ke Ijebu, da Ćarfe 2:00 na rana.
A ranar Litinin, a kan babbar titin Ijebu Ode zuwa Ibadan a mahaÉar âyan gudun hijira, Oru Ijebu.
âA yayin atisayen, jamiâan sun cafke Kadir Owolabi wanda ke kan babur, inda aka gudanar da bincike a kan jakunkunansa, an gano wasu kan mutane guda uku.
âBincike na farko ya kai ga kama wani wanda ake zargi, mai suna Jamiu Yisa, mai shekara 53, a bayan sakatariyar Ćaramar hukumar Ijebu Ode,â in ji ta.
Odutola ta ce, Kwamishinan âyan sanda jihar, Lanre Ogunlowo ya umurci hukumar binciken manyan laifuka ta jihar da ta Éauki ragamar lamarin domin gudanar da bincike mai zurfi.
Kakakin rundunar ta Ćara da cewa, rundunar ta sake jaddada aniyarta na Éaukar Ćwararan matakai na yaĆi da miyagun laifuka, ta kuma buĆaci mazauna yankin da su ba âyan sanda haÉin kai tare da ba jamaâa tabbacin amincewa da su da kuma basu kariyar sirri.
DW