DSS da Sojoji sun kashe ‘yan bindiga 50, sun ceto waɗanda aka sace a jihar Niger

DSS da Sojoji sun kashe ‘yan bindiga 50, sun ceto waɗanda aka sace a jihar Niger 

Rundunar DSS tare da Sojojin Najeriya sun yi babban nasara a jihar Neja, inda suka kashe sama da ‘yan bindiga 50 tare da ceto mutanen da aka sace a ƙauyen Kumbashi, karamar hukumar Mariga, a ranar Talata 26 ga Agusta.

Shaidu sun ce kusan ‘yan bindiga 300 dauke da manyan makamai suka kai hari da misalin ƙarfe 3 na rana, inda suka nufi sansanin DSS da ke yankin. Sai dai jami’an tsaro sun yi musu luguden wuta, suka fatattake su, inda wasu da dama suka tsere da rauni

Nagarifmradio

Comment As:

Comment (0)