Gurfanar da Jaafar Jaafar a Kotu Saboda Ya Binciko Badakalar N6.5B Ya Nuna Gwamnatin Kano Ta Gaza Inji Lauya Abba Hikima
- By NAGARIFMNEWS --
- Friday, 29 Aug, 2025

- 299 views
Gurfanar da Jaafar Jaafar a Kotu Saboda Ya Binciko Badakalar N6.5B Ya Nuna Gwamnatin Kano Ta Gaza Inji Lauya Abba Hikima
Fitaccen Éan jarida, Jaâafar Jaâafar, Zai gurfana a gaban kotu bisa tuhumar wallafa rahoton badakalar naira biliyan 6.5 da ake zargin Protocol na Gwamnan Jihar Kano. Abba Rogo
Tuhumar ta haifar da cece-kuce a fagen siyasa da alâumma, inda lauyoyi da masu rajin kare hakkin bilâadama suka bayyana damuwarsu kan yadda ake amfani da kotu wajen tsoratar da âyan jarida.
Barista Abba Hikima Fagge, shahararren lauya kuma mai kare hakkin bilâadama, ya bayyana cewa gurfanar da Jaâafar ba wai kawai batu ne na shariâa ba, illa kuwa ya fito fili ya nuna irin lalacewar tsarin mulki da gwamnatin Kano ta fada ciki.
âIdan gwamnati ta mayar da kotu makamin murkushe gaskiya, to wannan alama ce ta gazawa da lalacewar shugabanci. Abin da ake yi wa Jaâafar Jaâafar ba wai shariâa ba ce, illa dai yunĆurin rufe bakin gaskiya da hana alâumma jin abin da ke faruwa,â in ji shi.




