Jihar Kebbi
Gwamna Idris ya rantsar da sabon Kwamishina, ya Ćaddamar da Hukumar Raya Maâadanai
- By NAGARIFMNEWS --
- Tuesday, 16 Sep, 2025

- 225 views
Gwamna Idris ya rantsar da sabon Kwamishina, ya Ćaddamar da Hukumar Raya Maâadanai
Gwamnan Jihar Kebbi, Kwamared Dr. Nasir Idris (Kauran Gwandu), ya rantsar da Hon. Garba Hassan Warrah a matsayin sabon Kwamishinan Raya Maâadanai da Maâadinai.
Haka kuma, Gwamnan ya Ćaddamar da sabuwar Hukumar Raya Maâadanai ta Jihar Kebbi, tare da naÉa Abdullahi Buhari Warrah a matsayin Darakta Janar na hukumar.
Sabon Kwamishinan, Hon. Garba Hassan Warrah, ya maye gurbin Alhaji Haliru Aliyu Muhammad Wasagu, wanda Gwamnan ya dakatar.
An gudanar da rantsarwar ne a ranar Litinin, a Fadar Gwamnati da ke Birnin Kebbi, inda Babban Alkalin Jihar, Mai Shariâa Umar Abubakar, ya gabatar da rantsuwar a gaban Gwamna Nasir Idris.
Gwamna Idris ya taya sabbin jamiâan murna, yana mai bayyana wannan lokaci a matsayin tarihi. Ya ce an zaÉe su ne bisa cancanta da tarihin aiki, kuma gwamnatinsa ba za ta lamunci sakaci ko rashin aiki daga wani jamiâi ba.
âIna da yakinin nagartar ku, shi yasa muka ba ku wannan nauyi. Amma idan kuka kasa, za mu sallame ku,â in ji Gwamnan.
Ya jaddada cewa babban aikin sabon kwamishinan da hukumar ita ce haÉaka kuÉaÉen shiga ga jihar.
Nagarifmradio




