Yan Bindiga Sun Nemi A Gina Musu Makarantu, Asibitoci Da Filayen Kiwo a Matsayin Yarjejeniyar Sasanci
- By NAGARIFMNEWS --
- Thursday, 18 Sep, 2025

- 101 views
Yan Bindiga Sun Nemi A Gina Musu Makarantu, Asibitoci Da Filayen Kiwo a Matsayin Yarjejeniyar Sasanci,â Inji Gwamnatin KatsinaÂ
Gwamnatin Jihar Katsina ta tabbatar da cewa âyan bindiga da ke sassan jihar sun gabatar da wasu buĆatu a yayin tattaunawar zaman lafiya da alâummomin yankunan jihar.
Kwamishinan Tsaro na jihar, Nasiru Muâazu ne ya shaida wa BBC Hausa cewa cikin buĆatun akwai a gina makarantu, a gina asibitoci, da kuma samar da filayen kiwo ga makiyaya.
A cewarsa, ba gwamnatin Katsina bace ta fara tattaunawa da âyan bindigar, Ra'ayin shugabannin alâumma a Ćananan hukumomin Dan Musa, Jibiya, Batsari, Kankara, Kurfi da Musawa ne, da suka nemi hanyar sulhu don kawo Ćarshen kashe-kashe, satar shanu da garkuwa da mutane da aka dade ana fama da su.
Muâazu ya bayyana cewa rushewar shirin afuwar da gwamnatin baya ta aiwatar ne ya taÉarÉare lamarin tsaro, inda hare-haren suka yawaita daga Ćananan hukumomi guda 5 tsakanin 2011 da 2015 zuwa shekarar 2023.
Rahoton kamfanin bincike na tsaro, Beacon Consulting, ya nuna cewa a watannin farko na 2025 kaÉai, mutane 341 aka kashe, 495 kuma aka sace a hare-hare 247 da suka auku a Katsina.
A watan Yuli da ya gabata, gwamnatin jihar ta sanar da sabon shiri na gyara da kuma koya wa âyan bindiga da suka ajiye makamai ilimin addini da na zamani, tare da horo a sanaâoâi, domin su sake komawa cikin alâumma ba tare da cutarwa ba.
Sai dai makon da ya gabata, gwamnati ta gudanar da babban taro domin nazarin halin tsaro a jihar. An tabbatar cewa gwamnati za ta yi ĆoĆari wajen cika wasu daga cikin buĆatun âyan bindigar domin a samu dawwamammen zaman lafiya.
BBC




