Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Bindiga, Kachalla Maidawa, da Wasu 35..
- By NAGARIFMNEWS --
- Monday, 06 Oct, 2025

- 216 views
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Bindiga, Kachalla Maidawa, da Wasu 35..
Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da kashe fitaccen shugaban âyan bindiga, Kachalla Maidawa, tare da mutane 35 daga cikin tawagarsa a jerin hare-haren da suka Éauki mako Éaya a jihohin Arewa maso Yamma.
Wata sanarwa daga rundunar Defence Headquarters (DHQ) ta bayyana cewa sojoji sun gudanar da samame a wurare da dama ciki har da Katsina, Zamfara, Kaduna da Sokoto, inda suka lalata maboyar âyan taâadda, suka kwato bindigogi da motocin yaki.
âAn kashe Kachalla Maidawa, wanda ya jima yana addabar alâumma da sace-sacen mutane, fashi da kashe-kashe. Rundunar ta kuma kama wasu daga cikin mabiyansa da dama,â in ji DHQ.
Rahotanni sun ce Kachalla Maidawa yana Éaya daga cikin manyan shugabannin âyan bindiga da ke da alaÆa da ISWAP da sauran Æungiyoyin taâaddanci, kuma an daÉe ana nema saboda hare-haren da suka kashe daruruwan mutane a yankin.
Sojojin sun bayyana cewa za su ci gaba da bincike da sintiri a dazukan Arewa maso Yamma, tare da nufin kare rayukan alâumma da dawo da zaman lafiya.
 âBa za mu tsaya ba har sai mun tabbatar da cewa babu wani wuri da âyan taâadda ke samun mafaka,â in ji kakakin rundunar.
Nagarifmradio




