Abuja
Yan ta’adda sunce zasu tashi Bama-bamai a majalisar wakilan Najeriya.
Yan ta’adda sunce zasu tashi Bama-bamai a majalisar wakilan Najeriya.
Shugaban kwamitin majalisar mai kula da harkokin tsaron cikin gida Garba Muhammad a yau Talata ya bayyana cewa majalisar dokokin kasar ta samu barazanar ‘yan ta’adda na kai bama-bamai a harabar ginin tare da yin kira da a gaggauta yi wa ginin katangar baya a matsayin wani mataki na kare kai.
Garba ya bayyana hakan ne a Abuja a wajen wani taron jin ra’ayin jama’a kan kudirin kafa hukumar tsaro ta majalisar, wanda ke neman inganta harkokin tsaro, da kare ‘yan majalisa da ma’aikata da masu ziyara a majalisar dokokin kasar.Â
Jaridar Punch ta rawaito cewar Ginin da ya kunshi Majalisar Dattawa, Majalisar Wakilai da ofisoshi daban-daban, a cewarsa, yana fuskantar kalubalen tsaro da suka hada da matsalar satar motoci da babura, barna, katin shaida na bogi, da kuma kutsawa daga maziyartan da ba su yi rajista ba.
Nagarifmradio




