Wasu Fusatattun Matasa Sun Farmaki Tawagar Gwamnan Neja
- By NAGARIFMNEWS --
- Sunday, 02 Nov, 2025

- 102 views
Wasu Fusatattun Matasa Sun Farmaki Tawagar Gwamnan Neja
Wasu matasa a garin Bida, Jihar Neja, sun kai hari kan tawagar Gwamnan jihar, Umar Bago, inda suka lalata motocin gwamnati da dama tare da jikkata wasu jamiâan gwamnati, kamar yadda jaridar Starnews ta ruwaito.
Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne sakamakon fusata da matasan suka yi kan alkawarin da gwamnan ya yi musu na raba kuÉi ga alâumma a wani shiri da ake yi gabanin gudanar da zaÉukan Ćananan hukumomi a jihar.
Sai dai a cewar wasu daga cikin matasan, an ci amanarsu, domin a cewarsu, ââyan tsiraru ne kawai daga cikinmu suka samu kuÉin da aka raba,â abin da ya tayar musu da Ćura har ta kai ga tashin hankali.
Shaidu sun ce jamiâan tsaro sun yi ĆoĆarin shawo kan lamarin, amma rigimar ta riga ta Éarke kafin a samu daidaito. An kuma ce gwamnatin jihar ta tabbatar da faruwar lamarin tare da nuna takaici, tana mai cewa za a gudanar da bincike domin gano waÉanda suka haddasa tashin hankalin.
Nagarifmradio




