
Farfesa Usman Yusuf ya ce gwamnoni na boye wa Shugaba Bola Tinubu gaskiya game da halin tsananin wahalar da ake ciki a Najeriya.
Tsohon shugaban hukumar inshorar lafiyar ƙasa (NHIS), Farfesa Usman Yusuf, ya zargi gwamnoni da jawo matsaloli a Najeriya.
Â
Farfesa Usman Yusuf ya ce gwamnoni na boye wa Shugaba Bola Tinubu gaskiya game da halin tsananin wahalar da ake ciki a Najeriya.
Â
Farfesan ya bayyana hakane a wata hira da ta yi a wani gidan talabijin, yana mai cewa gwamnoni na karɓar kuɗaɗe masu yawa a ƙarƙashin gwamnatin Tinubu, amma ba'a ga wani abin a-zo-a-gani da suke yi da kuɗin ba.
Â
Ya ce sama da kashi 80 cikin 100 na matsalolin ƙasar gwamnoni ne ke jawo su, saboda sun gaza amfani da albarkatun da aka tanadar wa jama’arsu.