Yan bindiga sun kashe mutane biyu kauyen Dudaye, karamar hukumar Augie a jahar Kebbi.

Maudu’i Korafi Kan Matsalar Tsaro a Karamar Hukumar Augiu 

‎

‎Mai Girma Gwamna, 

‎

‎Ina rubuto wannan takarda ne don nuna matukar damuwa da bakin ciki game da halin rashin tsaro da ake fuskanta a Karamar Hukumar Augie. Lamarin ya kai wani mataki mai tayar da hankali, musamman da yawaitar hare-haren 'yan bindiga da sace-sacen mutane. 

‎

‎Wani Al’amari na Musamman:

‎A ranar 30 ga Agusta, 2025, a kauyen Dudaye, mutane biyu sun rasa rayukansu sakamakon harin 'yan bindiga. 

‎

‎Tasirin Lamarin

‎Mutane da dama sun bar gidajensu 

‎Harkokin kasuwanci sun tsaya cik 

‎Tsoro da firgici sun mamaye zukatan jama'a 

Nagarifmradio

Comment As:

Comment (0)