Matsalar yunwa

Matsalar yunwar ta fi ƙamari ne a Arewa-maso-Gabashin ƙasar, inda aka yi ƙiyasin cewa iyalai miliyan 2.3 suka tarwatse a cikin shekara 16 na rikicin Boko Haram.

Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce kimanin mutum miliyan 31 ne ke fuskantar ƙarancin abinci a Najeriya, wanda hakan ne mafi yawa a tarihi, sanadiyyar rage kudin tallafi da Amurka da sauran ƙasashen Yamma ke bayarwa.
 
Matsalar yunwar ta fi ƙamari ne a Arewa-maso-Gabashin ƙasar, inda aka yi ƙiyasin cewa iyalai miliyan 2.3 suka tarwatse a cikin shekara 16 na rikicin Boko Haram.
 
A baya, Amurka ce take bayar da kashi 60 cikin ɗari na tallafin jin-ƙai a Najeriya; sai dai, shugaba Donald Trump ya dakatar da tallafin. A yanzu, ƙasashen Yamma sun mayar da hankali wajen kashe kuɗi kan tsaro sanadiyyar barazana daga Rasha.
 
A sanadiyyar haka, ala tilas Najeriya ta zabtare kuɗin da take kasaftawa na tallafin jin-ƙai daga dala miliyan 910 zuwa dala miliyan 300.
 
Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce rikici, sauyin yanayi da matsin tattalin arziƙi da ambaliyar ruwa sun ƙara munana matsalar ƙarancin abinci.

Nagarifmradio

Comment As:

Comment (0)