An shiga fargaba da rudani a garin Izom da ke karamar hukumar Gurara, Jihar Neja
- By NAGARIFMNEWS --
- Friday, 14 Nov, 2025

- 50 views
An shiga fargaba da rudani a garin Izom da ke karamar hukumar Gurara, Jihar Neja, bayan wata tankar mai ta fadi kuma ta kama da wuta.
Lamarin ya faru da misalin karfe 8 na dare, inda direban tankar ya rasa iko da motar yayin da yake kokarin kaucewa ramuka a tsakiyar hanya.
Wani mazaunin garin, Mohammed Adamu, ya bayyana cewa ma’aikatan kashe gobara suna kokarin shawo kan wutar da ke ci har zuwa karfe 8:30 na dare. Ya ce babu wanda ya rasa ran sa, amma akwai gidaje kusa da wurin da gobarar ta faru, lamarin da ke kara tayar da hankali.
Har ila yau, gobarar ta haddasa cunkoso a bangarorin biyu na hanyar.
Shugaban Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja, Abdullahi Baba Arah, ya ce bai samu cikakken bayani kan lamarin ba a lokacin da aka tuntube shi




