Ƙungiyar Likitoci Masu Neman Ƙwarewa ta Najeriya, (NARD), ta dakatar da yajin aikin sai baba-ta-gani da ta fara kwana 29 da suka gabata.
- By NAGARIFMNEWS --
- Monday, 01 Dec, 2025

- 77 views
Ƙungiyar Likitoci Masu Neman Ƙwarewa ta Najeriya, (NARD), ta dakatar da yajin aikin sai baba-ta-gani da ta fara kwana 29 da suka gabata.
Â
Cikin wata sanarwa da shugaban ƙungiyar na ƙasa, Muhammad Sulaiman ya wallafa a shafinsa an X ranar Asabar da daddare ya ce ƙungiyar ta ɗauki matakin ne a zaman majalisar zartarwarta.
Â
Muhammad Suleiman ya ce ƙungiyar ta dakatar da yajin ne na tsawon mako huɗu, sakamakon cimma wasu yarjejeniyoyi da gwamnatin Najeriya kan buƙatun ƙungiyar 19.
Â
Ya ƙara da cewa ana sa ran kammala cimma manyan batutuwan da suka janyo yajin aikin - irin su biyan kuɗin ƙarin matsayi da bashin albashi da mambobin ƙungiyar ke bin gwamnati da aiwatar da biyan alawus na musamman - nan da mako biyu masu zuwa.
Â
Yajin aikin likitocin ya jefa wasu asibitin ƙasar cikin matsaloli daban-daban, inda marasa lafiya ke kokawa da rashin likitoci a wasu asibitocin ƙasar.




