ACP Kundi Dauda Ya Tsallake Rijiya da Baya a Harin Kwanton Bauna a Jigawa
- By NAGARIFMNEWS --
- Tuesday, 23 Dec, 2025

- 16 views
ACP Kundi Dauda Ya Tsallake Rijiya da Baya a Harin Kwanton Bauna a Jigawa
Â
Wani Mataimakin Kwamishinan ’Yan Sanda a Jihar Jigawa, ACP Kundi Dauda Abubakar, ya tsira da ransa bayan da ya samu rauni sakamakon harbin kibiya a wani harin kwanton bauna da ’yan bindiga suka kai wa tawagar ’yan sanda.
Â
Harin ya faru ne a yayin da jami’an ’yan sanda ke gudanar da samame a wani maboyar ’yan bindiga da ke yankin Atuman Fulani, a Karamar Hukumar Jahun, bisa bayanan sirri da suka shafi wasu da ake zargi da kai hare-hare a yankin.
Â
A wata sanarwa da rundunar ’yan sandan ta fitar, ta bayyana cewa ACP Kundi ya samu kulawar gaggawa a Babban Asibitin Jahun, kuma yanzu yana samun sauƙi. Rundunar ta kuma ce an harbi wasu daga cikin ’yan bindigar yayin arangamar, amma suka arce da raunuka.
Â
An kuma bayyana cewa jami’an tsaro na ci gaba da bin sawun ’yan bindigar da kuma ƙoƙarin kwato wasu bindigu da suka kasance a hannunsu.
Nagarifmradio




